Skip to content
Zakariya 1:18-21

Zakariya 1:18-21

18
Sa’an nan na dubi sama a gabana kuwa sai ga ƙahoni huɗu!
19
Na tambayi mala’ikan da yake mini magana, na ce, “Mene ne waɗannan?” Ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda, Isra’ila da kuma Urushalima.”
20
Sa’an nan Ubangiji ya nuna mini maƙera guda huɗu.
21
Na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan suke zuwa yi?” Ya amsa ya ce, “Waɗannan ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda har ba wanda yake iya ɗaga kansa, amma maƙeran sun zo don su tsorata su su kuma saukar da ƙahonin ƙasashen nan waɗanda suka ɗaga ƙahoninsu gāba da ƙasar Yahuda don su warwatsa ta.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options