Romawa 9:14-16
14
Me za mu ce ke nan? Allah marar adalci ne? Sam, ko kaɗan!
15
Gama ya ce wa Musa, “Zan nuna jinƙai ga wanda zan nuna jinƙai, zan kuma ji tausayin wanda zan ji tausayi.”
16
Saboda haka, bai danganta ga sha’awar mutum ko ƙoƙarinsa ba, sai dai ga jinƙan Allah.