Zum Inhalt springen
Romawa 8:22-25

Romawa 8:22-25

22
Mun san cewa dukan halitta tana nishi sai ka ce mace mai naƙuda har yă zuwa wannan lokaci.
23
Ba haka kaɗai ba ma, mu kanmu da muke da nunan fari na Ruhu, muna nishi a ciki-cikinmu yayinda muke jira da marmari a maishe mu ’ya’yan riƙo na Allah, fansar jikunanmu.
24
Gama a wannan begen ne muka sami ceto. Amma begen da ake gani ba bege ba ne sam. Wa yake begen abin da ya riga ya samu?
25
Amma in muna begen abin da ba mu riga mun samu tukuna ba, mukan jira da haƙuri.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options