Romawa 2:6-8
6
Allah, “Zai sāka wa kowane mutum gwargwadon aikin da ya yi.”
7
Ga waɗanda ta wurin naciya suna yin nagarta suna neman ɗaukaka, girma da rashin mutuwa, su za a ba su rai madawwami.
8
Amma ga waɗanda suke sonkai waɗanda suke ƙin gaskiya suke kuma bin mugunta, akwai fushi da haushi dominsu.