Romawa 2:17-24
17
To, kai, da kake kiran kanka mutumin Yahuda; in kana dogara ga doka kana kuma taƙama da dangantakarka da Allah;
18
in ka san nufinsa ka kuma amince da abin da yake mafifici domin an koyar da kai bisa ga doka;
19
in ka tabbata cewa kai jagora ne ga makafi, haske ga waɗanda suke cikin duhu,
20
mai koyar da masu wauta, malamin jarirai, domin a cikin dokar ce akwai sani da gaskiya
21
to, kai mai koya wa waɗansu, ba kanka kake koya wa ba? Kai da kake wa’azi kada a yi sata, kana sata?
22
Kai da kake cewa wa mutane kada su yi zina, kana yin zina? Kai da kake ƙyamar gumaka, kana wa haikali fashi?
23
Kai da kake taƙama da doka, kana nuna rashin bangirma ga Allah ta wurin karya dokar?
24
Kamar yadda yake a rubuce, “Ana saɓon sunan Allah a cikin Al’ummai saboda ku.”
Settings