Skip to content
Romawa 11:25-29

Romawa 11:25-29

25
Ba na so ku kasance cikin rashin sani game da wannan asirin ’yan’uwa, domin kada ku ɗaga kai. Isra’ila sun ɗanɗana sashe na taurarewa har sai da shigowar Al’ummai masu yawa ya cika.
26
Ta haka kuwa za a ceci dukan Isra’ila, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mai ceto zai zo daga Sihiyona; zai kawar da rashin bin Allah daga Yaƙub.
27
Wannan kuwa shi ne alkawarina da su sa’ad da na ɗauke musu zunubansu.”
28
Game da zancen nan na bishara kuwa, su abokan gāba ne saboda ku; amma game da zaɓen kuwa, su ƙaunatattunsa ne, albarkacin kakannin kakanninsu,
29
gama kyautar Allah da kiransa ba a sokewa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options