Zabura 94:2-7
2
Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
3
Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
4
Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
5
Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
6
Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
7
Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
Settings