Zabura 89:30-34
30
“In ’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
31
in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
32
zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
33
amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
34
Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
Settings