Skip to content
Zabura 89:29-37

Zabura 89:29-37

29
Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
30
“In ’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
31
in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
32
zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
33
amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
34
Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
35
Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
36
cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
37
zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” Sela
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options