Zabura 89:20-29
20
Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
21
Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
22
Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
23
Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
24
Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
25
Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
26
Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
27
Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
28
Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
29
Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
Settings