Allah da mutum sun yashe ni
14
Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
15
Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
16
Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
17
Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
18
Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.
Settings