Zabura 88:14-18
14
Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
15
Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
16
Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
17
Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
18
Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.
Settings