1
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na ’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ka nuna wa ƙasarka alheri, ya Ubangiji; ka mai da nasarorin Yaƙub.
2
Ka gafarta laifin mutanenka ka kuma shafe dukan zunubansu. Sela
3
Ka kau da dukan fushinka ka kuma juye daga hasalar fushinka.