Skip to content
Zabura 84:8-12

Zabura 84:8-12

8
Ka ji addu’ata, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka saurare ni, ya Allah na Yaƙub. Sela
9
Ka dubi garkuwarmu, ya Allah; ka duba da alheri a kan shafaffenka.
10
Rana guda a filayen gidan sun fi dubu a wani wuri dabam; zan gwammaci in zama mai tsaron ƙofa a gidan Allahna da in zauna a tentunan mugaye.
11
Gama Ubangiji Allah rana ne da kuma garkuwa; Ubangiji yakan yi alheri da kuma daraja; ba ya hana kowane abu mai kyau wa waɗanda suke aikata abin da yake daidai.
12
Ya Ubangiji Maɗaukaki, mai albarka ne mutumin da ya dogara gare ka.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options