Zabura 78:60-64
60
Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
61
Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
62
Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
63
Wuta ta cinye matasansu maza, ’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
64
aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
Settings