Skip to content
Zabura 72:1-7

Zabura 72:1-7

1
Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
2
Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
3
Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
4
Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece ’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
5
Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
6
Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
7
A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options