Zabura 7:11-16
11
Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
12
In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
13
Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
14
Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
15
Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
16
Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
Settings