Zabura 66:5-7
5
Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
6
Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
7
Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada ’yan tawaye su tayar masa. Sela