Skip to content
Zabura 47:1-4

Zabura 47:1-4

1
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta ’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
2
Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
3
Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
4
Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. Sela
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options