Zabura 41:10-13
10
Amma kai, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, ka tā da ni, don in sāka musu.
11
Na sani kana jin daɗina, gama abokin gābana ba zai ci nasara a kaina ba.
12
Cikin mutuncina ka riƙe ni ka sa ni a gabanka har abada.
13
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, har abada abadin.