Skip to content
Zabura 38:15-20

Zabura 38:15-20

15
Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
16
Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
17
Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
18
Na furta laifina; na damu da zunubina.
19
Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
20
Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options