Zabura 38:15-20
15
Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
16
Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
17
Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
18
Na furta laifina; na damu da zunubina.
19
Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
20
Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
Settings