Zabura 37:9-11
9
Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
10
A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
11
Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.