Skip to content
Zabura 30:1-5

Zabura 30:1-5

1
Zabura ce. Wata waƙa. Don keɓewar haikali. Ta Dawuda. Zan girmama ka Ya Ubangiji, gama ka tsamo ni daga zurfafa ba ka bar abokan gābana sun yi farin ciki a kaina ba.
2
Ya Ubangiji Allahna, na yi kira gare ka don taimako ka kuwa warkar da ni.
3
Ya Ubangiji, ka dawo da ni daga kabari; ka kiyaye ni daga gangarawa zuwa cikin rami.
4
Ku rera ga Ubangiji, ku tsarkakansa; ku yabi sunansa mai tsarki.
5
Gama fushinsa na ɗan lokaci ne amma alherinsa har matuƙa ne; mai yiwuwa a yi kuka da dare amma farin ciki kan zo da safe.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options