Zabura 23:1-4
1
Zabura ta Dawuda. Ubangiji ne yake kiwona, ba zan rasa kome ba,
2
Yakan sa in kwanta a makiyaya mai ɗanyar ciyawa, yakan bi da ni kusa da ruwaye marar hayaniya,
3
yakan maido da raina. Yakan bi da ni a hanyoyin adalci saboda sunansa.
4
Ko da na yi tafiya ta kwari na inuwar mutuwa, ba zan ji tsoron mugu ba, gama kana tare da ni; bulalarka na dūka da kuma sandanka na tafiya, za su yi mini ta’aziyya.
Settings