Skip to content
Zabura 21:8-12

Zabura 21:8-12

8
Hannunka zai kakkama dukan abokan gābanka; hannunka na dama zai kakkama masu ƙinka.
9
A lokacin bayyanarka za ka sa su zama kamar wutar matoya. Cikin fushinsa Ubangiji zai haɗiye su, kuma wutarsa za tă cinye su.
10
Za ka hallaka ’ya’yansu daga duniya, zuriyarsu kuma daga ’yan adam.
11
Ko da yake suna shirya maka mugunta suna kuma ƙirƙiro mugayen dabaru, ba za su yi nasara ba;
12
gama za ka sa su juye bayansu sa’ad da ka auna su da bakan da ka ja.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options