Zabura 18:20-24
20
Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
21
Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
22
Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
23
Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
24
Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
Settings