Zabura 147:16-18
16
Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
17
Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
18
Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.