Zabura 147:1-3
1
Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
2
Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
3
Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.