Zabura 147:1-6
1
Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
2
Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
3
Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
4
Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
5
Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
6
Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
Settings