Skip to content
Zabura 145:14-20

Zabura 145:14-20

14
Ubangiji yana riƙe da dukan waɗanda suka faɗi yana kuma ɗaga dukan waɗanda aka rusunar da su ƙasa.
15
Idanun kowa yana dogara gare ka, kana kuma ba su abincinsu a lokacin da ya dace.
16
Ka buɗe hannunka ka kuma ƙosar da sha’awar kowane abu mai rai.
17
Ubangiji mai adalci ne cikin dukan hanyoyinsa yana kuma nuna ƙauna ga dukan abubuwan da ya yi.
18
Ubangiji yana kusa da kowa da ya kira gare shi, ga duk wanda ya kira gare shi cikin gaskiya.
19
Yakan cika sha’awar waɗanda suke tsoronsa; yakan ji kukansu yă kuma cece su.
20
Ubangiji yakan lura da dukan waɗanda suke ƙaunarsa, amma dukan mugaye zai hallaka su.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options