Zabura 135:8-12
8
Ya kashe ’ya’yan fari na Masar, ’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
9
Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
10
Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
11
Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
12
ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
Settings