15
Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
16
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
17
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
18
Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.