Zabura 132:13-17
13
Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
14
“Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
15
zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
16
Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
17
“A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
Settings