Zabura 132:11-18
11
Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
12
in ’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to ’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
13
Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
14
“Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
15
zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
16
Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
17
“A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
18
Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”
Settings