Zabura 109:2-5
2
gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
3
Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
4
A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
5
Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.