Zabura 107:35-41
35
Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
36
a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
37
Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
38
ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
39
Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
40
shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
41
Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
Settings