Zabura 106:40-46
40
Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
41
Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
42
Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
43
Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
44
Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
45
saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
46
Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
Settings