Skip to content
Zabura 105:28-32

Zabura 105:28-32

28
Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
29
Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
30
Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
31
Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
32
Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options