Zabura 105:23-25
23
Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
24
Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
25
waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.