Zabura 105:17-20
17
ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
18
Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
19
sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
20
Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya ’yantar da shi.