Skip to content
Zabura 105:16-22

Zabura 105:16-22

16
Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
17
ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
18
Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
19
sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
20
Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya ’yantar da shi.
21
Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
22
don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options