Skip to content
Zabura 104:10-23

Zabura 104:10-23

10
Ya sa maɓulɓulai suka zuba ruwa cikin kwaruruka; yana gudu tsakanin duwatsu.
11
Suna ba da ruwa ga dukan namun jeji; jakunan jeji suna kashe ƙishirwansu.
12
Tsuntsaye sarari suna sheƙunansu kusa da ruwan; suna rera cikin rassa.
13
Yana wa duwatsu banruwa daga ɗakinsa na sama; ƙasa tana ƙoshiya da amfanin aikinsa.
14
Yana sa ciyawa tă yi girma saboda shanu, tsire-tsire domin mutum ya nome, suna fid da abinci daga ƙasa,
15
ruwan inabi yakan sa zuciyar mutum tă yi murna, mai kuwa yakan sa fuska tă yi haske, abinci kuma da yake riƙe zuciyarsa.
16
Ana yi wa itatuwan Ubangiji banruwa sosai, al’ul na Lebanon da ya shuka.
17
A can tsuntsaye suke sheƙunnansu; shamuwa tana da gidanta a itatuwan fir.
18
Manyan duwatsu na awakin jeji ne; tsagaggun duwatsun mafaka ne ga rema.
19
Wata ne ke ƙididdigar lokuta, rana kuma ta san sa’ad da za tă fāɗi.
20
Ka yi duhu, sai ya zama dare, sai dukan namun jeji a kurmi suka fito a maƙe.
21
Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta suna kuma neman abincinsu daga Allah.
22
Rana ta fito, sai suka koma shiru; suka koma suka kwanta a kogwanninsu.
23
Mutum yakan tafi aikinsa, zuwa wurin aikinsa har yamma.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options