Tsarin dare da rana
19
Wata ne ke ƙididdigar lokuta, rana kuma ta san sa’ad da za tă fāɗi.
20
Ka yi duhu, sai ya zama dare, sai dukan namun jeji a kurmi suka fito a maƙe.
21
Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta suna kuma neman abincinsu daga Allah.
22
Rana ta fito, sai suka koma shiru; suka koma suka kwanta a kogwanninsu.
23
Mutum yakan tafi aikinsa, zuwa wurin aikinsa har yamma.
Settings