Zabura 104:1-9
1
Yabi Ubangiji, ya raina. Ya Ubangiji Allahna, kana da girma ƙwarai; kana saye da daraja da ɗaukaka.
2
Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga ya shimfiɗa sammai kamar tenti
3
ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye. Ya maido da gizagizai suka zama keken yaƙinsa yana hawa a kan fikafikan iska.
4
Ya mai da iska suka zama ’yan saƙonsa harsunan wuta kuma bayinsa.
5
Ya kafa duniya a kan tussanta; ba za a iya matsar da ita ba.
6
Ka rufe ta da zurfi kamar da riga ruwaye sun tsaya a bisa duwatsu.
7
Amma a tsawatawarka ruwaye suka gudu da jin ƙarar tsawanka suka ruga da gudu;
8
suka gudu a bisa duwatsu, suka gangara zuwa cikin kwaruruka, zuwa wurin da ka shirya musu.
9
Ka kafa iyakar da ba a iya tsallakawa; ba za su ƙara rufe duniya ba.
Settings