Zabura 102:24-27
24
Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
25
A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
26
Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
27
Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
Settings