Skip to content
Zabura 102:23-28

Zabura 102:23-28

23
Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
24
Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
25
A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
26
Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
27
Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
28
’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options