Skip to content
Karin Magana 8:1-11

Karin Magana 8:1-11

1
Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
2
A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
3
kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
4
“Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan ’yan adam.
5
Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
6
Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
7
Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
8
Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
9
Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
10
Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
11
gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options