मुख्य मजकुरावर जा
Karin Magana 7:13-21

Karin Magana 7:13-21

13
Sai ta kama shi ta rungume shi da duban soyayya a fuskarta ta ce,
14
“Ina da hadaya ta salama a gida; yau zan cika alkawarina.
15
Saboda haka na fito don in sadu da kai; na neme ka na kuma same ka!
16
Na lulluɓe gadona da lili masu launi dabam-dabam daga Masar.
17
Na yayyafa turare a gadona da mur, aloyes da kuma kirfa.
18
Zo, mu sha zurfin ƙauna har safe; bari mu ji wa ranmu daɗi da ƙauna!
19
Mijina ba ya gida; ya yi tafiya mai nisa.
20
Ya ɗauki jakarsa cike da kuɗi ba zai kuwa dawo gida ba sai tsakiyar wata.”
21
Da kalmomin rarrashi ta sa ya kauce; ta ɗauki hankalinsa da sulɓin maganarta.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options