Karin Magana 5:11-14
11
A ƙarshen rayuwarku za ku yi ta nishi, sa’ad da namanku da jikinku suka zagwanye.
12
Za ku ce, “Me ya sa na ƙi horo! Me ya sa zuciyata ta ƙi gyara!
13
Ban yi biyayya da malamaina ba ko in saurari masu koyar da ni.
14
Na zo gab da hallaka gaba ɗaya a tsakiyar dukan taron.”