Karin Magana 19:25-29
25
Ka bulale mai ba’a, marasa azanci kuwa za su yi la’akari; ka tsawata wa mai basira, zai kuwa ƙara sani.
26
Duk wanda ya yi wa mahaifinsa fashi ya kuma kori mahaifiyarsa ɗa ne da kan kawo kunya da wulaƙanci.
27
In ka daina jin umarni, ɗana, za ka kuwa kauce daga kalmomin sani.
28
Mai shaidar da yake malalaci yana wa shari’a ba’a ne, bakin mugaye kuma na haɗiye mugunta.
29
An shirya tara saboda masu ba’a ne, dūka kuma saboda bayan wawaye.
Settings