Skip to content
Ƙidaya 3:14-20

Ƙidaya 3:14-20

14
Ubangiji ya yi magana da Musa a Hamadar Sinai ya ce,
15
“Ka ƙidaya Lawiyawa bisa ga iyalansu da kabilarsu. Ka ƙidaya kowane ɗan jinjiri mai wata ɗaya ko fiye.”
16
Saboda haka Musa ya ƙidaya su duka, kamar yadda maganar Ubangiji ta umarta.
17
Ga sunayen ’ya’yan Lawi, Gershon, Kohat da Merari.
18
Ga sunayen mutanen Gershon, Libni, da Shimeyi
19
Sunayen mutanen Kohat kuwa su ne, Amram, Izhar, Hebron da Uzziyel.
20
Dangin Merari su ne. Mali da Mushi. Ga kabilan Lawiyawa bisa ga iyalansu.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options